< Zabura 36 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
El pecado del malhechor dice en su corazón: No hay temor del Señor ante sus ojos.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
Porque se consuela pensando que su pecado no será descubierto ni aborrecido.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
En las palabras de su boca están el mal y el engaño; él ha dejado de ser sabio y hacer el bien.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
Él piensa en el mal sobre su cama; toma un camino que no es bueno; él no es un enemigo del mal.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Tu misericordia, oh Señor, llega hasta los cielos, y tu fidelidad alcanza hasta las nubes.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Tu justicia es como los montes de Dios; tu juicio es como el gran abismo; Oh Señor, le cuidas al hombre y a la bestia.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
¡Cuán buena es tu amorosa misericordia, oh Dios! los hijos de los hombres se esconden bajo la sombra de tus alas.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
Las delicias de tu casa serán derramadas sobre ellos; les darás de beber del río de tus placeres.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
Porque contigo está la fuente de la vida; en tu luz veremos la luz.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Ojalá no haya fin en tu amorosa misericordia para con los que te conocen, ni tu justicia para con los rectos de corazón.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Que el pie del orgullo no venga contra mí, ni la mano de los malvados me saque de mi lugar.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
Allí han descendido los hacedores del mal; han sido humillados y no se levantarán.

< Zabura 36 >