< Zabura 36 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
La transgresión del impío habla a su corazón. No hay temor a ʼElohim delante de sus ojos.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
Se jacta ante sus propios ojos De que su iniquidad no será descubierta ni aborrecida.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
Las palabras de su boca son iniquidad y engaño. Dejó de ser sabio, de hacer el bien.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
Trama iniquidad sobre su cama. Se mantiene en camino no bueno. No aborrece lo malo.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Oh Yavé, tu misericordia llega hasta el cielo, Y hasta las nubes tu fidelidad.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Tu justicia es como las montañas de ʼEL, Tus juicios, como inmenso abismo. Tú, oh Yavé, preservas al hombre y la bestia.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
¡Oh ʼElohim, cuán preciosa es tu misericordia! Por eso los hombres se amparan bajo la sombra de tus alas.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
Son plenamente saciados con la abundancia de tu casa, Les das de beber del torrente de tus delicias.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
Porque contigo está el manantial de la vida. En tu luz vemos la luz.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Extiende tu misericordia a los que te conocen, Y tu justicia a los rectos de corazón.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
No me alcance el pie de la soberbia, Ni me mueva la mano del inicuo.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
Ahí cayeron los que obran iniquidad, Fueron derribados, Y no pueden levantarse.