< Zabura 36 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
برای رهبر سرایندگان. مزمور داوود، خدمتگزار خداوند. گناه در عمق دل انسان شرور لانه کرده است و هیچ ترسی از خدا ندارند.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
او چنان از خود راضی است که نمی‌تواند گناهش را ببیند و از آن رویگردان شود.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
سخنانش شرارت‌آمیز و مملو از دروغ است؛ حکمت و نیکی در وجودش نیست.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
به راههای کج می‌رود و از کارهای خلاف دست نمی‌کشد.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
محبت تو، ای خداوند، تا به آسمانها می‌رسد و وفاداری تو به بالاتر از ابرها!
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
عدالت تو همچون کوههای بزرگ پابرجاست؛ احکام تو مانند دریا عمیق است. ای خداوند، تو حافظ انسانها و حیوانات هستی.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
خدایا، محبت تو چه عظیم است! آدمیان زیر سایهٔ بالهای تو پناه می‌گیرند.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
آنها از برکت خانهٔ تو سیر می‌شوند و تو از چشمهٔ نیکویی خود به آنها می‌نوشانی.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
تو سرچشمهٔ حیات هستی؛ از نور تو است که ما نور حیات را می‌بینیم!
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
خداوندا، محبت تو همیشه بر کسانی که تو را می‌شناسند باقی بماند و نیکویی تو پیوسته همراه راست‌دلان باشد.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
نگذار متکبران به من حمله کنند و شروران مرا متواری سازند.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
ببینید چگونه بدکاران افتاده‌اند! آنها نقش زمین شده‌اند و دیگر نمی‌توانند برخیزند!

< Zabura 36 >