< Zabura 36 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
Til sangmesteren; av Herrens tjener, av David. Syndens ord til den ugudelige er i mitt hjertes innerste. Det er ikke gudsfrykt for hans øine.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
For en smigrer ham i hans øine ved å finne hans synd, ved å hate ham.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
Hans munns ord er urett og svik; han har latt av å fare viselig frem, å gjøre godt.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
Han optenker urett på sitt leie, han stiller sig på en vei som ikke er god; det onde hater han ikke.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Herre! til himmelen når din miskunnhet, din trofasthet inntil skyene.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Din rettferdighet er som veldige fjell, dine dommer er et stort dyp; mennesker og dyr frelser du, Herre!
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
Hvor kostelig er din miskunnhet, Gud! Menneskenes barn søker ly i dine vingers skygge.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
De mettes overflødig av ditt huses fedme, og av dine gleders strøm gir du dem å drikke.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
For hos dig er livets kilde, i ditt lys ser vi lys.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
La din miskunnhet vare ved for dem som kjenner dig, og din rettferdighet for de opriktige av hjertet.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
La ikke den overmodiges fot komme over mig og ikke de ugudeliges hånd jage mig bort!
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
Der faller de som gjør urett; de blir støtt ned og kan ikke reise sig.