< Zabura 36 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
Au chef des chantres. Du serviteur de l’Éternel, de David. La parole impie du méchant est au fond de son cœur; La crainte de Dieu n’est pas devant ses yeux.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
Car il se flatte à ses propres yeux, Pour consommer son iniquité, Pour assouvir sa haine.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
Les paroles de sa bouche sont fausses et trompeuses; Il renonce à agir avec sagesse, à faire le bien.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
Il médite l’injustice sur sa couche, Il se tient sur une voie qui n’est pas bonne, Il ne repousse pas le mal.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Éternel! Ta bonté atteint jusqu’aux cieux, Ta fidélité jusqu’aux nues.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Ta justice est comme les montagnes de Dieu, Tes jugements sont comme le grand abîme. Éternel! Tu soutiens les hommes et les bêtes.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
Combien est précieuse ta bonté, ô Dieu! A l’ombre de tes ailes les fils de l’homme cherchent un refuge.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
Ils se rassasient de l’abondance de ta maison, Et tu les abreuves au torrent de tes délices.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
Car auprès de toi est la source de la vie; Par ta lumière nous voyons la lumière.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Étends ta bonté sur ceux qui te connaissent, Et ta justice sur ceux dont le cœur est droit!
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Que le pied de l’orgueil ne m’atteigne pas, Et que la main des méchants ne me fasse pas fuir!
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
Déjà tombent ceux qui commettent l’iniquité; Ils sont renversés, et ils ne peuvent se relever.

< Zabura 36 >