< Zabura 36 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
To the chief Musician, [A Psalm] of David the servant of the LORD. The transgression of the wicked saith within my heart, [that there is] no fear of God before his eyes.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
For he flattereth himself in his own eyes, until his iniquity be found to be hateful.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
The words of his mouth [are] iniquity and deceit: he hath left off to be wise, [and] to do good.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
He deviseth mischief upon his bed; he setteth himself in a way [that is] not good; he abhorreth not evil.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Thy mercy, O LORD, [is] in the heavens; [and] thy faithfulness [reacheth] unto the clouds.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Thy righteousness [is] like the great mountains; thy judgments [are] a great deep: O LORD, thou preservest man and beast.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
How excellent [is] thy lovingkindness, O God! therefore the children of men put their trust under the shadow of thy wings.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
They shall be abundantly satisfied with the fatness of thy house; and thou shalt make them drink of the river of thy pleasures.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
For with thee [is] the fountain of life: in thy light shall we see light.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
O continue thy lovingkindness unto them that know thee; and thy righteousness to the upright in heart.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Let not the foot of pride come against me, and let not the hand of the wicked remove me.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
There are the workers of iniquity fallen: they are cast down, and shall not be able to rise.