< Zabura 36 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
For the Leader. A Psalm of David the servant of the LORD. Transgression speaketh to the wicked, methinks — there is no fear of God before his eyes.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
For it flattereth him in his eyes, until his iniquity be found, and he be hated.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
The words of his mouth are iniquity and deceit; he hath left off to be wise, to do good.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
He deviseth iniquity upon his bed; he setteth himself in a way that is not good; he abhorreth not evil.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Thy lovingkindness, O LORD, is in the heavens; Thy faithfulness reacheth unto the skies.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Thy righteousness is like the mighty mountains; Thy judgments are like the great deep; man and beast Thou preservest, O LORD.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
How precious is Thy lovingkindness, O God! and the children of men take refuge in the shadow of Thy wings.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
They are abundantly satisfied with the fatness of Thy house; and Thou makest them drink of the river of Thy pleasures.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
For with Thee is the fountain of life; in Thy light do we see light.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
O continue Thy lovingkindness unto them that know Thee; and Thy righteousness to the upright in heart.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Let not the foot of pride overtake me, and let not the hand of the wicked drive me away.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
There are the workers of iniquity fallen; they are thrust down, and are not able to rise.