< Zabura 36 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
For the end, by David the servant of the Lord. The transgressor, that he may sin, says within himself, [that] there is no fear of God before his eyes.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
For he has dealt craftily before him, to discover his iniquity and hate it.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
The words of his mouth are transgression and deceit: he is not inclined to understand [how] to do good.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
He devises iniquity on his bed; he gives himself to every evil way; and does not abhor evil.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
O Lord, your mercy is in the heaven; and your truth [reaches] to the clouds.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Your righteousness is as the mountains of God, your judgements are as a great deep: O Lord, you will preserve men and beasts.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
How have you multiplied your mercy, O God! so the children of men shall trust in the shelter of your wings.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
They shall be fully satisfied with the fatness of your house; and you shall cause them to drink of the full stream of your delights.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
For with you is the fountain of life: in your light we shall see light.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Extend your mercy to them that know you; and your righteousness to the upright in heart.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Let not the foot of pride come against me, and let not the hand of sinners move me.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
There have all the workers of iniquity fallen: they are cast out, and shall not be able to stand.