< Zabura 36 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
For the choirmaster. A Psalm of David, the servant of the LORD. An oracle is in my heart regarding the transgression of the wicked man: There is no fear of God before his eyes.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
For his eyes are too full of conceit to detect or hate his own sin.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
The words of his mouth are wicked and deceitful; he has ceased to be wise and well-doing.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
Even on his bed he plots wickedness; he sets himself on a path that is not good; he fails to reject evil.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Your loving devotion, O LORD, reaches to the heavens, Your faithfulness to the clouds.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Your righteousness is like the highest mountains; Your judgments are like the deepest sea. O LORD, You preserve man and beast.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
How precious is Your loving devotion, O God, that the children of men take refuge in the shadow of Your wings!
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
They feast on the abundance of Your house, and You give them drink from Your river of delights.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
For with You is the fountain of life; in Your light we see light.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Extend Your loving devotion to those who know You, and Your righteousness to the upright in heart.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Let not the foot of the proud come against me, nor the hand of the wicked drive me away.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
There the evildoers lie fallen, thrown down and unable to rise.