< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
ダビデがアビメレクの前で狂ったさまをよそおい、追われて出ていったときの歌 わたしは常に主をほめまつる。そのさんびはわたしの口に絶えない。
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
わが魂は主によって誇る。苦しむ者はこれを聞いて喜ぶであろう。
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
わたしと共に主をあがめよ、われらは共にみ名をほめたたえよう。
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
わたしが主に求めたとき、主はわたしに答え、すべての恐れからわたしを助け出された。
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
主を仰ぎ見て、光を得よ、そうすれば、あなたがたは、恥じて顔を赤くすることはない。
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
この苦しむ者が呼ばわったとき、主は聞いて、すべての悩みから救い出された。
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
主の使は主を恐れる者のまわりに陣をしいて彼らを助けられる。
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
主の恵みふかきことを味わい知れ、主に寄り頼む人はさいわいである。
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
主の聖徒よ、主を恐れよ、主を恐れる者には乏しいことがないからである。
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
若きししは乏しくなって飢えることがある。しかし主を求める者は良き物に欠けることはない。
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
子らよ、来てわたしに聞け、わたしは主を恐るべきことをあなたがたに教えよう。
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
さいわいを見ようとして、いのちを慕い、ながらえることを好む人はだれか。
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
あなたの舌をおさえて悪を言わせず、あなたのくちびるをおさえて偽りを言わすな。
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
悪を離れて善をおこない、やわらぎを求めて、これを努めよ。
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
主の目は正しい人をかえりみ、その耳は彼らの叫びに傾く。
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
主のみ顔は悪を行う者にむかい、その記憶を地から断ち滅ぼされる。
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
正しい者が助けを叫び求めるとき、主は聞いて、彼らをそのすべての悩みから助け出される。
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
主は心の砕けた者に近く、たましいの悔いくずおれた者を救われる。
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
正しい者には災が多い。しかし、主はすべてその中から彼を助け出される。
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
主は彼の骨をことごとく守られる。その一つだに折られることはない。
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
悪は悪しき者を殺す。正しい者を憎む者は罪に定められる。
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
主はそのしもべらの命をあがなわれる。主に寄り頼む者はひとりだに罪に定められることはない。

< Zabura 34 >