< Karin Magana 1 >
1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
ダビデの子、イスラエルの王ソロモンの箴言。
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
これは人に知恵と教訓とを知らせ、悟りの言葉をさとらせ、
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
賢い行いと、正義と公正と公平の教訓をうけさせ、
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
思慮のない者に悟りを与え、若い者に知識と慎みを得させるためである。
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
賢い者はこれを聞いて学に進み、さとい者は指導を得る。
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
人はこれによって箴言と、たとえと、賢い者の言葉と、そのなぞとを悟る。
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
主を恐れることは知識のはじめである、愚かな者は知恵と教訓を軽んじる。
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
わが子よ、あなたは父の教訓を聞き、母の教を捨ててはならない。
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
それらは、あなたの頭の麗しい冠となり、あなたの首の飾りとなるからである。
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
わが子よ、悪者があなたを誘っても、それに従ってはならない。
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
彼らがあなたに向かって、「一緒に来なさい。われわれは待ち伏せして、人の血を流し、罪のない者を、ゆえなく伏してねらい、
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
陰府のように、彼らを生きたままで、のみ尽し、健やかな者を、墓に下る者のようにしよう。 (Sheol )
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
われわれは、さまざまの尊い貨財を得、奪い取った物で、われわれの家を満たそう。
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
あなたもわれわれの仲間に加わりなさい、われわれは共に一つの金袋を持とう」と言っても、
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
わが子よ、彼らの仲間になってはならない、あなたの足をとどめて、彼らの道に行ってはならない。
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
彼らの足は悪に走り、血を流すことに速いからだ。
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
すべて鳥の目の前で網を張るのは、むだである。
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
彼らは自分の血を待ち伏せし、自分の命を伏してねらうのだ。
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
すべて利をむさぼる者の道はこのようなものである。これはその持ち主の命を取り去るのだ。
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
知恵は、ちまたに呼ばわり、市場にその声をあげ、
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
城壁の頂で叫び、町の門の入口で語る。
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
「思慮のない者たちよ、あなたがたは、いつまで思慮のないことを好むのか。あざける者は、いつまで、あざけり楽しみ、愚かな者は、いつまで、知識を憎むのか。
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
わたしの戒めに心をとめよ、見よ、わたしは自分の思いを、あなたがたに告げ、わたしの言葉を、あなたがたに知らせる。
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
わたしは呼んだが、あなたがたは聞くことを拒み、手を伸べたが、顧みる者はなく、
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
かえって、あなたがたはわたしのすべての勧めを捨て、わたしの戒めを受けなかったので、
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
わたしもまた、あなたがたが災にあう時に、笑い、あなたがたが恐慌にあう時、あざけるであろう。
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
これは恐慌が、あらしのようにあなたがたに臨み、災が、つむじ風のように臨み、悩みと悲しみとが、あなたがたに臨む時である。
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
その時、彼らはわたしを呼ぶであろう、しかし、わたしは答えない。ひたすら、わたしを求めるであろう、しかし、わたしに会えない。
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
彼らは知識を憎み、主を恐れることを選ばず、
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
わたしの勧めに従わず、すべての戒めを軽んじたゆえ、
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
自分の行いの実を食らい、自分の計りごとに飽きる。
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
思慮のない者の不従順はおのれを殺し、愚かな者の安楽はおのれを滅ぼす。
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
しかし、わたしに聞き従う者は安らかに住まい、災に会う恐れもなく、安全である」。