< Zabura 26 >

1 Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
Dawid dwom. Bu me bem, Awurade, efisɛ, mabɔ bra a asɛm nni ho: mede me ho too Awurade so na manhinhim.
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
Sɔ me hwɛ, Awurade, hwehwɛ me koma ne mʼadwene mu.
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
Wʼadɔe wɔ mʼanim daa na mɛnantew wo nokware mu.
4 Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
Me ne nnaadaafo ntena na me ne nyaatwomfo nso nni hwee yɛ.
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
Mikyi nnebɔneyɛfo guabɔ na mempɛ sɛ me ne amumɔyɛfo tena.
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
Mehohoro me nsa wɔ bembu mu, na mekɔ wʼafɔremuka ho ahyia, Awurade,
7 ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
na mepae mu ka wʼayeyi na meka wʼanwonwade nyinaa.
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
Mʼani gye ofi a wote mu ho, Awurade, faako a wʼanuonyam wɔ no.
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
Mfa me kra nka nnebɔneyɛfo de ho nkɔ, ne me nkwa nka mogyapɛfo de ho,
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
wɔn a amumɔyɛ nhyehyɛe wɔ wɔn nsam na adanmude ayɛ wɔn nsa nifa ma.
11 Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
Nanso mebɔ ɔbra a ho tew; hu me mmɔbɔ na gye me nkwa.
12 Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.
Mʼanan sisi asase tamaa so; na guabɔ kɛse ase na mɛkamfo Awurade.

< Zabura 26 >