< Zabura 26 >
1 Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
Júzgame, o! Jehová, porque yo en mi integridad he andado, y en Jehová he confiado: no vacilaré.
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
Pruébame, o! Jehová, y tiéntame: funde mis riñones y mi corazón.
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
Porque tu misericordia está delante de mis ojos: y en tu verdad ando.
4 Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
No me asenté con los varones de falsedad: ni entré con los que andan encubiertamente.
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
Aborrecí la congregación de los malignos: y con los impíos nunca me asenté.
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
Lavaré en inocencia mis manos: y andaré al derredor de tu altar, o! Jehová,
7 ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
Para dar voz de alabanza, y para contar todas tus maravillas.
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
Jehová, la habitación de tu casa he amado: y el lugar del tabernáculo de tu gloria.
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
No juntes con los pecadores mi alma, ni con los varones de sangres mi vida.
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
En cuyas manos está el mal hecho, y su diestra está llena de cohechos.
11 Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
Mas yo ando en mi integridad: redímeme, y ten misericordia de mí.
12 Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.
Mi pie ha estado en rectitud, y en las congregaciones bendeciré a Jehová.