< Zabura 26 >
1 Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
Dari Daud. Berilah keadilan kepadaku, ya TUHAN, sebab aku telah hidup dalam ketulusan; kepada TUHAN aku percaya dengan tidak ragu-ragu.
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
Ujilah aku, ya TUHAN, dan cobalah aku; selidikilah batinku dan hatiku.
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
Sebab mataku tertuju pada kasih setia-Mu, dan aku hidup dalam kebenaran-Mu.
4 Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
Aku tidak duduk dengan penipu, dan dengan orang munafik aku tidak bergaul;
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
aku benci kepada perkumpulan orang yang berbuat jahat, dan dengan orang fasik aku tidak duduk.
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
Aku membasuh tanganku tanda tak bersalah, lalu berjalan mengelilingi mezbah-Mu, ya TUHAN,
7 ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
sambil memperdengarkan nyanyian syukur dengan nyaring, dan menceritakan segala perbuatan-Mu yang ajaib.
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
TUHAN, aku cinta pada rumah kediaman-Mu dan pada tempat kemuliaan-Mu bersemayam.
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
Janganlah mencabut nyawaku bersama-sama orang berdosa, atau hidupku bersama-sama orang penumpah darah,
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
yang pada tangannya melekat perbuatan mesum, dan yang tangan kanannya menerima suapan.
11 Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
Tetapi aku ini hidup dalam ketulusan; bebaskanlah aku dan kasihanilah aku.
12 Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.
Kakiku berdiri di tanah yang rata; aku mau memuji TUHAN dalam jemaah.