< Zabura 26 >

1 Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
[A Psalm] of David. Judge me, O LORD, for I have walked in mine integrity: I have trusted also in the LORD without wavering.
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
Examine me, O LORD, and prove me; try my reins and my heart.
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
For thy lovingkindness is before mine eyes; and I have walked in thy truth.
4 Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
I have not sat with vain persons; neither will I go in with dissemblers.
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
I hate the congregation of evil-doers, and will not sit with the wicked.
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
I will wash mine hands in innocency; so will I compass thine altar, O LORD:
7 ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
That I may make the voice of thanksgiving to be heard, and tell of all thy wondrous works.
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
LORD, I love the habitation of thy house, and the place where thy glory dwelleth.
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
Gather not my soul with sinners, nor my life with men of blood:
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
In whose hands is mischief, and their right hand is full of bribes.
11 Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
But as for me, I will walk in mine integrity: redeem me, and be merciful unto me.
12 Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.
My foot standeth in an even place: in the congregations will I bless the LORD.

< Zabura 26 >