< Zabura 26 >

1 Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
“A psalm of David.” Be thou my judge, O LORD! for I have walked in uprightness. I have put my trust in the LORD, therefore shall I not fall.
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
Examine me, O LORD! and prove me; Try my reins and my heart!
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
For thy kindness is ever before my eyes, And I walk in thy truth.
4 Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
I sit not with men of falsehood. And go not in company with dissemblers.
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
I hate the assembly of evil-doers, And do not sit with the wicked.
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
I wash my hands in innocence. And go around thine altar. O LORD!
7 ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
To utter the voice of thanksgiving, And tell of all thy wondrous works.
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
O LORD! I love the habitation of thy house, The place where thine honor dwelleth!
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
Gather not my breath with sinners, Nor my life with men of blood,
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
In whose hands is mischief, And whose right hands are full of bribes!
11 Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
But as for me, I walk in my integrity; Oh, redeem me, and be merciful to me!
12 Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.
My feet tread in a straight path; In the congregation will I bless the LORD.

< Zabura 26 >