< Zabura 26 >
1 Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
A Psalme of David. Judge me, O Lord, for I haue walked in mine innocency: my trust hath bene also in the Lord: therefore shall I not slide.
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
Proue me, O Lord, and trie mee: examine my reines, and mine heart.
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
For thy louing kindnesse is before mine eyes: therefore haue I walked in thy trueth.
4 Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
I haue not hanted with vaine persons, neither kept companie with the dissemblers.
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
I haue hated the assemblie of the euill, and haue not companied with the wicked.
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
I will wash mine handes in innocencie, O Lord, and compasse thine altar,
7 ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
That I may declare with the voyce of thankesgiuing, and set foorth all thy wonderous woorkes.
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
O Lord, I haue loued the habitation of thine house, and the place where thine honour dwelleth.
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
Gather not my soule with the sinners, nor my life with the bloodie men:
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
In whose handes is wickednes, and their right hand is full of bribes.
11 Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
But I will walke in mine innocencie: redeeme me therefore, and be mercifull vnto me.
12 Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.
My foote standeth in vprightnesse: I will praise thee, O Lord, in the Congregations.