< Zabura 26 >

1 Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
Van David. Wees mijn Rechter, o Jahweh! Want mijn wandel is rein; Altijd heb ik op Jahweh vertrouwd, Nooit gewankeld!
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
Beproef mij, en toets mij, o Jahweh; Doorgrond mijn nieren en hart.
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
Want uw liefde houd ik voor ogen, En in uw waarheid heb ik geleefd;
4 Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
Ik heb geen gemeenschap met veinzers, Met gluipers ga ik niet om;
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
Ik haat het gezelschap der bozen, En met slechtaards zit ik niet aan.
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
Maar ik was mijn handen in onschuld, En sta rond uw altaar,
7 ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
O Jahweh, om U een loflied te zingen, En al uw wonderen te melden.
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
Jahweh, ik bemin het huis, waar Gij toeft, De woonplaats van uw heerlijkheid.
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
Werp mij niet weg met de zondaars, Mijn leven niet met moordenaars,
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
Aan wier handen misdaad kleeft, Wier rechterhand is omgekocht.
11 Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
Neen, ik wandel in onschuld; Red mij dus, Jahweh, en wees mij genadig!
12 Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.
Mijn voet staat in de gerechtigheid vast; Ik zal U loven, o Jahweh, in de volle gemeente!

< Zabura 26 >