< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Unto the end. A Psalm of David. To you, Lord, I have lifted up my soul.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
In you, my God, I trust. Let me not be put to shame.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
And do not let my enemies laugh at me. For all who remain with you will not be confounded.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
May all those who act unjustly over nothing be confounded. O Lord, demonstrate your ways to me, and teach me your paths.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Direct me in your truth, and teach me. For you are God, my Savior, and I remain with you all day long.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
O Lord, remember your compassion and your mercies, which are from ages past.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Do not remember the offenses of my youth and my ignorances. Remember me according to your mercy, because of your goodness, O Lord.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
The Lord is sweet and righteous. Because of this, he will grant a law to those who fall short in the way.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
He will direct the mild in judgment. He will teach the meek his ways.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
All the ways of the Lord are mercy and truth, to those who yearn for his covenant and his testimonies.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Because of your name, O Lord, you will pardon my sin, for it is great.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Which is the man who fears the Lord? He has established a law for him, on the way that he has chosen.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
His soul will dwell upon good things, and his offspring will inherit the earth.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
The Lord is a firmament to those who fear him, and his covenant will be made manifest to them.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
My eyes are ever toward the Lord, for he will pull my feet from the snare.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Look upon me and have mercy on me; for I am alone and poor.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
The troubles of my heart have been multiplied. Deliver me from my needfulness.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
See my lowliness and my hardship, and release all my offenses.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Consider my enemies, for they have been multiplied, and they have hated me with an unjust hatred.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Preserve my soul and rescue me. I will not be ashamed, for I have hoped in you.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
The innocent and the righteous have adhered to me, because I have remained with you.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Free Israel, O God, from all his tribulations.