< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
大衛的詩。 耶和華啊,我的心仰望你。
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
我的上帝啊,我素來倚靠你; 求你不要叫我羞愧, 不要叫我的仇敵向我誇勝。
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
凡等候你的必不羞愧; 惟有那無故行奸詐的必要羞愧。
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
耶和華啊,求你將你的道指示我, 將你的路教訓我!
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
求你以你的真理引導我,教訓我, 因為你是救我的上帝。 我終日等候你。
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
耶和華啊,求你記念你的憐憫和慈愛, 因為這是亙古以來所常有的。
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
求你不要記念我幼年的罪愆和我的過犯; 耶和華啊,求你因你的恩惠,按你的慈愛記念我。
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
耶和華是良善正直的, 所以他必指示罪人走正路。
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
他必按公平引領謙卑人, 將他的道教訓他們。
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
凡遵守他的約和他法度的人, 耶和華都以慈愛誠實待他。
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
耶和華啊,求你因你的名赦免我的罪, 因為我的罪重大。
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
誰敬畏耶和華, 耶和華必指示他當選擇的道路。
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
他必安然居住; 他的後裔必承受地土。
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
耶和華與敬畏他的人親密; 他必將自己的約指示他們。
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
我的眼目時常仰望耶和華, 因為他必將我的腳從網裏拉出來。
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
求你轉向我,憐恤我, 因為我是孤獨困苦。
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
我心裏的愁苦甚多, 求你救我脫離我的禍患。
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
求你看顧我的困苦,我的艱難, 赦免我一切的罪。
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
求你察看我的仇敵, 因為他們人多,並且痛痛地恨我。
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
求你保護我的性命,搭救我, 使我不致羞愧,因為我投靠你。
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
願純全、正直保守我, 因為我等候你。
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
上帝啊,求你救贖以色列脫離他一切的愁苦。

< Zabura 25 >