< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
För sångmästaren; en psalm av David. HERREN bönhöre dig på nödens dag, Jakobs Guds namn beskydde dig.
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Han sände dig hjälp från helgedomen, och stödje dig från Sion.
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Han tänke på alla dina spisoffer och upptage med välbehag ditt brännoffer. (Sela)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Han give dig vad ditt hjärta begär och fullborde alla dina rådslag.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Må vi få jubla över din seger och i vår Guds namn resa upp baneret; HERREN uppfylle alla dina böner.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Nu vet jag att HERREN giver seger åt sin smorde; han svarar honom från sin heliga himmel, genom väldiga gärningar giver hans högra hand seger.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
De andra prisa vagnar, de prisa hästar, men vi prisa HERRENS, vår Guds, namn.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
De sjunka ned och falla, men vi resa oss upp och bliva beståndande.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
HERRE, giv seger; ja, konungen svare oss på den tid då vi ropa.

< Zabura 20 >