< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
Gospod te sliši na dan stiske, ime Jakobovega Boga te brani,
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
pošlje ti pomoč iz svetišča in te okrepi s Siona,
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
spominja se vseh tvojih daritev in sprejema tvojo žgalno daritev. (Sela)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Usliši te glede na tvoje lastno srce in izpolni vso tvojo namero.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Veselili se bomo v tvoji rešitvi duše in svoje prapore bomo postavili v imenu svojega Boga. Gospod izpolnjuje vse tvoje prošnje.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Sedaj vem, da Gospod rešuje svojega maziljenca; iz svojih svetih nebes ga bo uslišal z rešujočo močjo svoje desnice.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Nekateri zaupajo v bojne vozove, nekateri pa v konje, toda mi se bomo spominjali imena Gospoda, svojega Boga.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Oni so ponižani in padli, toda mi vstanemo in stojimo pokončno.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Reši, Gospod. Naj nas sliši kralj, ko kličemo.

< Zabura 20 >