< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
Hanoiñ’azo an-tsan-kasotriañe t’Iehovà, hañonjoñ’ azo ankaboañe ey ty tahinan’ Añahare’ Iakobe.
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Hañitrifa’e imba boak’amy toe-miavakey hanohañ’ azo hirik’e Tsiône ao.
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Ho tiahi’e o enga-mahakama iabio, vaho hiantofa’e o fisoroña’oo! Selà
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Hatolots’ azo ze salalan’ arofo’o le ho henefeñe iaby o ereñere’oo.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Ho poñafe’ay rebeke ty fandrombaha’o, ty tahinan’Añahare’ay ro añelahelà’ay kobaiñe; ho henefa’ Iehovà abey o halali’oo.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Apotako henaneo, te ho rombahe’ Iehovà i noriza’ey; ho toiñe’e boak’ an-dindi’e masiñe ao, amy haozaram-pandrombaha’ i fitàn-kavana’eiy.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Miato an-tsarete o ila’eo, an-tsoavala ka ty ila’e; fa ho tiahi’ay ty tahina’ Iehovà Andrianañahare’ay.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Nibokoke iereo naho nikorovoke mitroatse zahay vaho mijohañe.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Rombaho, ry Iehovà; hanoiñe abey i mpanjakay te kanjie’ay!

< Zabura 20 >