< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
למנצח מזמור לדוד יענך יהוה ביום צרה ישגבך שם אלהי יעקב׃
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
ישלח עזרך מקדש ומציון יסעדך׃
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
יזכר כל מנחתך ועולתך ידשנה סלה׃
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
יתן לך כלבבך וכל עצתך ימלא׃
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
נרננה בישועתך ובשם אלהינו נדגל ימלא יהוה כל משאלותיך׃
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
עתה ידעתי כי הושיע יהוה משיחו יענהו משמי קדשו בגברות ישע ימינו׃
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
אלה ברכב ואלה בסוסים ואנחנו בשם יהוה אלהינו נזכיר׃
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
המה כרעו ונפלו ואנחנו קמנו ונתעודד׃
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
יהוה הושיעה המלך יעננו ביום קראנו׃

< Zabura 20 >