< Zabura 20 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
Auf den Siegesspender, ein Lied, von David. Der Herr erhöre dich noch an dem Tag der Not! Des Gottes Jakobs Name schütze dich!
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Er sende aus dem Heiligtum dir Hilfe und stütze dich von Sion her!
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Er nehme an all deine Opfergaben und freue sich an deinen Brandopfern! (Sela)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Er gebe dir, was nur dein Herz begehrt; und lasse alle deine Pläne wohl gelingen!
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Dann jauchzen wir ob deines Sieges und jubeln laut in unseres Gottes Namen. Der Herr erfülle dir die Wünsche all! -
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
jetzt weiß ich es: Der Herr hilft dem, den er gesalbt, erhört ihn von dem heiligen Himmel her mit hilfereichen Taten seiner Rechten.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Sind jene noch so stolz auf Wagen und auf Rosse, wir sind es auf den Namen unsres Herrn und Gottes.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Sie krümmen sich und stürzen hin; wir aber stehen wieder auf.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Herr, hilf dem Königund höre uns, sooft wir rufen!