< Zabura 20 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
[Dem Vorsänger. Ein Psalm von David.] Jehova erhöre dich am Tage der Drangsal, der Name des Gottes Jakobs setze dich in Sicherheit;
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Er sende deine Hülfe aus dem Heiligtum, und von Zion aus unterstütze er dich;
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Er gedenke aller deiner Speisopfer, und dein Brandopfer wolle er annehmen! (Sela)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Er gebe dir nach deinem Herzen, und alle deine Ratschläge erfülle er!
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Jubeln wollen wir über deine Rettung, und im Namen unseres Gottes das Panier erheben. [O. schwingen] Jehova erfülle alle deine Bitten!
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Jetzt weiß ich, daß Jehova seinen Gesalbten rettet; aus seinen heiligen Himmeln wird er ihn erhören durch die Machttaten des Heils seiner Rechten.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Diese gedenken der Wagen und jene der Rosse, wir aber gedenken [d. h. rühmend] des Namens Jehovas, unseres Gottes.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Jene krümmen sich und fallen, wir aber stehen und halten uns aufrecht.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Jehova, rette! Der König erhöre uns am Tage unseres Rufens!