< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
Pour la fin, psaume de David. Que le Seigneur vous exauce au jour de la tribulation; que le nom du Dieu de Jacob vous protège.
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Qu’il vous envoie du secours du lieu saint; et que de Sion il vous défende.
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Qu’il se souvienne de tous vos sacrifices, et que votre holocauste lui soit agréable.
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Qu’il vous rende selon votre cœur, et qu’il confirme tous vos desseins.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Nous nous réjouirons de votre salut; et dans le nom de notre Dieu nous nous glorifierons.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Que le Seigneur accomplisse toutes vos demandes; maintenant j’ai reconnu que le Seigneur a sauvé son Christ. Il l’exaucera du ciel, son sanctuaire: le salut de sa droite est puissant.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Ceux-ci se confient dans des chariots, et ceux-là dans des chevaux; mais nous, c’est le nom du Seigneur que nous invoquerons.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Ils ont été pris dans des lacs, et ils sont tombés; mais nous, nous nous sommes relevés et nous sommes restés debout,
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Seigneur, sauvez le roi, et exaucez-nous au jour où nous vous invoquerons.

< Zabura 20 >