< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
Psaume de David, [donné] au maître chantre. Que l'Eternel te réponde au jour que tu seras en détresse; que le nom du Dieu de Jacob te mette en une haute retraite.
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Qu'il envoie ton secours du saint lieu, et qu'il te soutienne de Sion.
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Qu'il se souvienne de toutes tes oblations, qu'il réduise en cendre ton holocauste; (Sélah)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Qu'il te donne ce que ton cœur désire, et qu'il fasse réussir tes desseins.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Nous triompherons de ta délivrance, et nous marcherons à enseignes déployées au Nom de notre Dieu; l'Eternel t'accordera toutes tes demandes.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Déjà je connais que l'Eternel a délivré son Oint; il lui répondra des Cieux de sa Sainteté; la délivrance faite par sa droite est avec force.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Les uns [se vantent] de leurs chariots, et les autres de leurs chevaux, mais nous nous glorifierons du Nom de l'Eternel notre Dieu.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Ceux-là ont ployé, et sont tombés; mais nous nous sommes relevés, et soutenus.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Eternel, délivre. Que le Roi nous réponde au jour que nous crierons.

< Zabura 20 >