< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
I desire that Yahweh will answer you [when you call out to him] when you have troubles! God is the one whom ([our ancestor] Jacob/the Israeli people) [worshiped]; I desire that he will protect you [MTY] [from being harmed by your enemies].
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
I desire/hope that he will reach out from his sacred temple and help you, and aid you from [where he lives] on Zion [Hill].
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
I desire/hope that he will accept all the offerings that you give him to be burned [on the altar], and all your [other] offerings.
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
I want him to give to you what you desire, and that you will be able to accomplish all that you desire to do.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
When [we hear that] you have defeated [your enemies], we will shout joyfully. We will lift up a banner proclaiming that it is God [MTY] [who helps us](inc). I want Yahweh to [do for you] all that you request him to do.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
I know now that Yahweh rescues [me], the one whom he has chosen [to be king]. From his holy place in heaven he will answer me, and he will save me by his great power [MTY].
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Some [kings] trust that because they have chariots [they will be able to defeat their enemies], and some trust that their horses [will enable them to defeat their enemies], but we will trust in the power [MTY] of Yahweh our God.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Some kings will stumble and fall down, but we will be strong and (not be moved/continue standing firm).
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Yahweh, enable [me], your king, to defeat our enemies! Answer us when we call out to you [to help us.]

< Zabura 20 >