< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
To the Chief Musician. A Melody of David. Yahweh answer thee, in the day of distress, The Name of the God of Jacob give thee safety;
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Send thy help out of the sanctuary, and, out of Zion, sustain thee;
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Remember every present of thine, and, thine ascending-sacrifice, esteem. (Selah)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Give thee according to thy heart, and, all thy purposes, fulfil.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
We will shout aloud in thy salvation, and, in the Name of our God, shall we become great, Yahweh fulfil all thy petitions.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Now, do I know that Yahweh, hath saved, his Anointed One, —He answereth him out of his holy heavens, by the mighty saving deeds of his own right hand.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
These, by chariots, and, those, by horses, but, we, by the Name of Yahweh our God, will prevail.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
They, have bowed down and fallen, but, we, have arisen, and stand upright.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Yahweh, hath saved the king. Answer us, then, on the day when we call.

< Zabura 20 >