< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
For the Leader. A Psalm of David. The LORD answer thee in the day of trouble; the name of the God of Jacob set thee up on high;
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Send forth thy help from the sanctuary, and support thee out of Zion;
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Receive the memorial of all thy meal-offerings, and accept the fat of thy burnt-sacrifice; (Selah)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Grant thee according to thine own heart, and fulfil all thy counsel.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
We will shout for joy in thy victory, and in the name of our God we will set up our standards; the LORD fulfil all thy petitions.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Now know I that the LORD saveth His anointed; He will answer him from His holy heaven with the mighty acts of His saving right hand.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Some trust in chariots, and some in horses; but we will make mention of the name of the LORD our God.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
They are bowed down and fallen; but we are risen, and stand upright.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Save, LORD; let the King answer us in the day that we call.

< Zabura 20 >