< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
To the chief music-maker. A Psalm. Of David. May the Lord give ear to you in the day of trouble; may you be placed on high by the name of the God of Jacob;
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
May he send you help from the holy place, and give you strength from Zion;
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
May he keep all your offerings in mind, and be pleased with the fat of your burned offerings; (Selah)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
May he give you your heart's desire, and put all your purposes into effect.
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
We will be glad in your salvation, and in the name of our God we will put up our flags: may the Lord give you all your requests.
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Now am I certain that the Lord gives salvation to his king; he will give him an answer from his holy heaven with the strength of salvation in his right hand.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Some put their faith in carriages and some in horses; but we will be strong in the name of the Lord our God.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
They are bent down and made low; but we have been lifted up.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Come to our help, Lord: let the king give ear to our cry.

< Zabura 20 >