< Zabura 20 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
Til Sangmesteren. En Salme af David.
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Paa Trængselens Dag bønhøre HERREN dig, værne dig Jakobs Guds Navn!
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Han sende dig Hjælp fra Helligdommen, fra Zion styrke han dig;
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
han komme alle dine Afgrødeofre i Hu og tage dit Brændoffer gyldigt! (Sela)
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
Han give dig efter dit Hjertes Attraa, han fuldbyrde alt dit Raad,
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
at vi maa juble over din Frelse, løfte Banner i vor Guds Navn! HERREN opfylde alle dine Bønner!
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Nu ved jeg, at HERREN frelser sin Salvede og svarer ham fra sin hellige Himmel med sin højres frelsende Vælde.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Nogle stoler paa Heste, andre paa Vogne, vi sejrer ved HERREN vor Guds Navn.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
De synker i Knæ og falder, vi rejser os og kommer atter paa Fode. HERRE, frels dog Kongen og svar os, den Dag vi kalder!

< Zabura 20 >