< Zabura 2 >

1 Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Зашто се буне народи и племена помишљају залудне ствари?
2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
Устају цареви земаљски, и кнезови се скупљају на Господа и на помазаника Његовог.
3 Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
"Раскинимо свезе њихове и збацимо са себе јарам њихов."
4 Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
Онај, што живи на небесима, смеје се, Господ им се подсмева.
5 Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
Па им говори у гневу свом и јарошћу својом збуњује их:
6 “Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
"Ја сам помазао цара свог на Сиону, на светој гори својој."
7 Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
Казаћу наредбу Господњу; Он рече мени: "Ти си син мој, ја те сад родих.
8 Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
Ишти у мене, и даћу ти народе у наследство, и крајеве земаљске теби у државу.
9 Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
Ударићеш их гвозденом палицом; разбићеш их као лончарски суд."
10 Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
Сад, цареви, оразумите се; научите се судије земаљске!
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
Служите Господу са страхом, и радујте се с трепетом.
12 Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Поштујте сина, да се не разгневи, и ви не изгинете на путу свом; јер ће се гнев Његов брзо разгорети. Благо свима који се у Њ уздају!

< Zabura 2 >