< Zabura 147 >
1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Aleluja! Hvalite Jahvu jer je dobar, pjevajte Bogu našem jer je sladak; svake hvale on je dostojan!
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Jahve gradi Jeruzalem, sabire raspršene Izraelce.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
On liječi one koji su srca skršena i povija rane njihove.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
On određuje broj zvijezda, svaku njezinim imenom naziva.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Velik je naš Gospodin i svesilan, nema mjere mudrosti njegovoj.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Jahve pridiže ponizne, zlotvore do zemlje snizuje.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Pjevajte Jahvi pjesmu zahvalnu, svirajte na citari Bogu našem!
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Oblacima on prekriva nebesa i zemlji kišu sprema; daje da po bregovima raste trava i bilje na službu čovjeku.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
On stoci hranu daje i mladim gavranima kada grakću.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Za konjsku snagu on ne mari nit' mu se mile bedra čovječja.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Mili su Jahvi oni koji se njega boje, koji se uzdaju u dobrotu njegovu.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Slavi Jahvu, Jeruzaleme, hvali Boga svoga, Sione!
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
On učvrsti zasune vrata tvojih, blagoslovi u tebi tvoje sinove.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
On dade mir granicama tvojim, pšenicom te hrani najboljom.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Besjedu svoju šalje na zemlju, brzo trči riječ njegova.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Kao vunu snijeg razbacuje, prosipa mraz poput pepela.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
On sipa grÓad kao zalogaje, voda mrzne od njegove studeni.
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Riječ svoju pošalje i vode se tope; dunu vjetrom i vode otječu.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Riječ svoju on objavi Jakovu, odluke svoje i zakone Izraelu.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Ne učini tako nijednom narodu: nijednom naredbe svoje ne objavi! Aleluja!