< Zabura 140 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
To the chief Musician. A Psalm of David. Free me, O Jehovah, from the evil man; preserve me from the violent man:
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
Who devise mischiefs in [their] heart; every day are they banded together for war.
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
They sharpen their tongues like a serpent; adders' poison is under their lips. (Selah)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Keep me, O Jehovah, from the hands of the wicked [man], preserve me from the violent man, who devise to overthrow my steps.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
The proud have hidden a snare for me, and cords; they have spread a net by the way-side; they have set traps for me. (Selah)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
I have said unto Jehovah, Thou art my God: give ear, O Jehovah, to the voice of my supplications.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
Jehovah, the Lord, is the strength of my salvation: thou hast covered my head in the day of battle.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
Grant not, O Jehovah, the desire of the wicked; further not his device: they would exalt themselves. (Selah)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
[As for] the head of those that encompass me, let the mischief of their own lips cover them.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Let burning coals fall on them; let them be cast into the fire; into deep waters, that they rise not up again.
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
Let not the man of [evil] tongue be established in the earth: evil shall hunt the man of violence to [his] ruin.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
I know that Jehovah will maintain the cause of the afflicted one, the right of the needy.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Yea, the righteous shall give thanks unto thy name; the upright shall dwell in thy presence.

< Zabura 140 >