< Zabura 137 >
1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
Babil ırmakları kıyısında oturup Siyon'u andıkça ağladık;
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
Çevredeki kavaklara Lirlerimizi astık.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
Çünkü orada bizi tutsak edenler bizden ezgiler, Bize zulmedenler bizden şenlik istiyor, “Siyon ezgilerinden birini okuyun bize!” diyorlardı.
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Nasıl okuyabiliriz RAB'bin ezgisini El toprağında?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Ey Yeruşalim, seni unutursam, Sağ elim kurusun.
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Seni anmaz, Yeruşalim'i en büyük sevincimden üstün tutmazsam, Dilim damağıma yapışsın!
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Yeruşalim'in düştüğü gün, “Yıkın onu, yıkın temellerine kadar!” Diyen Edomlular'ın tavrını anımsa, ya RAB.
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Ey sen, yıkılası Babil kızı, Bize yaptıklarını Sana ödetecek olana ne mutlu!
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Ne mutlu senin yavrularını tutup Kayalarda parçalayacak insana!