< Zabura 137 >
1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
David Hieremiae super flumina Babylonis illic sedimus et flevimus cum recordaremur Sion
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
in salicibus in medio eius suspendimus organa nostra
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
quia illic interrogaverunt nos qui captivos duxerunt nos verba cantionum et qui abduxerunt nos hymnum cantate nobis de canticis Sion
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
quomodo cantabimus canticum Domini in terra aliena
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
si oblitus fuero tui Hierusalem oblivioni detur dextera mea
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
adhereat lingua mea faucibus meis si non meminero tui si non praeposuero Hierusalem in principio laetitiae meae
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
memor esto Domine filiorum Edom diem Hierusalem qui dicunt exinanite exinanite usque ad fundamentum in ea
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
filia Babylonis misera beatus qui retribuet tibi retributionem tuam quam retribuisti nobis
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
beatus qui tenebit et adlidet parvulos tuos ad petram