< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
Psalmus David, Jeremiæ. [Super flumina Babylonis illic sedimus et flevimus, cum recordaremur Sion.
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
In salicibus in medio ejus suspendimus organa nostra:
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
quia illic interrogaverunt nos, qui captivos duxerunt nos, verba cantionum; et qui abduxerunt nos: Hymnum cantate nobis de canticis Sion.
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Quomodo cantabimus canticum Domini in terra aliena?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Si oblitus fuero tui, Jerusalem, oblivioni detur dextera mea.
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Adhæreat lingua mea faucibus meis, si non meminero tui; si non proposuero Jerusalem in principio lætitiæ meæ.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Memor esto, Domine, filiorum Edom, in die Jerusalem: qui dicunt: Exinanite, exinanite usque ad fundamentum in ea.
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Filia Babylonis misera! beatus qui retribuet tibi retributionem tuam quam retribuisti nobis.
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Beatus qui tenebit, et allidet parvulos tuos ad petram.]

< Zabura 137 >