< Zabura 137 >
1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
An den Wassern zu Babel saßen wir und weinten, wenn wir an Zion gedachten.
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
Unsere Harfen hingen wir an die Weiden, die daselbst sind.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
Denn dort hießen uns singen, die uns gefangen hielten, und in unserm Heulen fröhlich sein: “Singet uns ein Lied von Zion!”
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Wie sollten wir des HERRN Lied singen in fremden Landen?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Vergesse ich dein, Jerusalem, so werde ich meiner Rechten vergessen.
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Meine Zunge soll an meinem Gaumen kleben, wo ich nicht dein gedenke, wo ich nicht lasse Jerusalem meine höchste Freude sein.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
HERR, gedenke der Kinder Edom den Tag Jerusalems, die da sagten: “Rein ab, rein ab bis auf ihren Boden!”
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Du verstörte Tochter Babel, wohl dem, der dir vergilt, wie du uns getan hast!
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Wohl dem, der deine jungen Kinder nimmt und zerschmettert sie an dem Stein!