< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
Sur les fleuves de Babylone, là nous nous sommes assis, et nous avons pleuré, comme nous nous souvenions de Sion.
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
Aux saules, au milieu d’elle, nous avons suspendu nos instruments.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
Parce que là ceux qui nous avaient emmenés captifs, nous demandèrent les paroles de nos chants;
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Comment chanterons-nous un cantique du Seigneur dans une terre étrangère?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Si je t’oublie, Jérusalem, que ma main droite soit livrée à l’oubli.
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Que ma langue s’attache à mon gosier, si je ne me souviens pas de toi,
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Souvenez-vous, Seigneur, des fils d’Edom au jour de Jérusalem,
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Fille malheureuse de Babylone, bienheureux celui qui te rendra la rétribution de ce que tu nous a fait!
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Bienheureux celui qui saisira et brisera tes petits enfants contre la pierre!

< Zabura 137 >