< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
When we [had been taken to] Babylonia, [far from Jerusalem], we sat down by the rivers there, and we cried when we thought about [the temple on] Zion [Hill in Jerusalem].
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
On the willow trees [alongside the rivers] we hung our harps [because we did not want to play them any more because we were very sad].
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
The [soldiers] who had captured us [and taken us to Babylonia] told us to sing [for them]; they told us to (entertain them/make them happy), saying, “Sing for us one of the songs [that you previously sang in] Jerusalem!”
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
But [we thought], “We [are sad because we have been punished by Yahweh and brought to this] foreign land, so we cannot [RHQ] sing songs about Yahweh while we are here!”
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
If I forget about Jerusalem [APO], Iet my right hand wither [with the result that I will be unable to play my harp]
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Do not allow me to sing again [MTY], if I forget about Jerusalem, if I do not consider that Jerusalem causes me to be more joyful than anything else does.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Yahweh, [punish] the people of the Edom people-group for what they did on the day that the army of Babylon captured Jerusalem. Do not forget that they said, “Tear down all the buildings! Destroy them completely! Leave only the foundations!”
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
And you people of Babylon, you will certainly be destroyed! Those who punish you in return for what you did to us will be happy;
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
they will take your babies and completely smash them on the rocks.

< Zabura 137 >