< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
Upon the rivers of Babylon, there we sat and wept: when we remembered Sion:
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
On the willows in the midst thereof we hung up our instruments.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
For there they that led us into captivity required of us the words of songs. And they that carried us away, said: Sing ye to us a hymn of the songs of Sion.
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
How shall we sing the song of the Lord in a strange land?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
If I forget thee, O Jerusalem, let my right hand be forgotten.
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Let my tongue cleave to my jaws, if I do not remember thee: If I make not Jerusalem the beginning of my joy.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Remember, O Lord, the children of Edom, in the day of Jerusalem: Who say: Rase it, rase it, even to the foundation thereof.
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
O daughter of Babylon, miserable: blessed shall he be who shall repay thee thy payment which thou hast paid us.
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Blessed be he that shall take and dash thy little ones against the rock.

< Zabura 137 >