< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
By the rivers of Babylon we were seated, weeping at the memory of Zion,
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
Hanging our instruments of music on the trees by the waterside.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
For there those who had taken us prisoners made request for a song; and those who had taken away all we had gave us orders to be glad, saying, Give us one of the songs of Zion.
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
How may we give the Lord's song in a strange land?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
If I keep not your memory, O Jerusalem, let not my right hand keep the memory of its art.
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
If I let you go out of my thoughts, and if I do not put Jerusalem before my greatest joy, let my tongue be fixed to the roof of my mouth.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
O Lord, keep in mind against the children of Edom the day of Jerusalem; how they said, Let it be uncovered, uncovered even to its base.
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
O daughter of Babylon, whose fate is destruction; happy is the man who does to you what you have done to us.
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Happy is the man who takes your little ones, crushing them against the rocks.

< Zabura 137 >