< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
Ved Babels Floder, der sad vi og græd, naar Zion randt os i Hu.
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
Vi hængte vore Harper i Landets Pile.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
Thi de, der havde bortført os, bad os synge, vore Bødler bad os være glade: »Syng os af Zions Sange!«
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Hvor kan vi synge HERRENS Sange paa fremmed Grund?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Jerusalem, glemmer jeg dig, da visne min højre!
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Min Tunge hænge ved Ganen, om ikke jeg ihukommer dig, om ikke jeg sætter Jerusalem over min højeste Glæde!
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
HERRE, ihukom Edoms Sønner for Jerusalems Dag, at de raabte: »Nedbryd, nedbryd lige til Grunden!«
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Du Babels Datter, du Ødelægger! Salig den, der gengælder dig, hvad du gjorde imod os!
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Salig den, der griber dine spæde og knuser dem mod Klippen!

< Zabura 137 >