< Zabura 137 >
1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
Ved Babylons Floder, der sad vi, og vi græd, naar vi kom Zion i Hu.
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
Paa Vidierne i Landet havde vi hængt vore Harper.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
Thi der begærede de, som holdt os fangne, at vi skulde synge; og de, som plagede os, begærede, at vi skulde være glade: „Synger for os af Zions Sange!”
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Hvorledes skulde vi synge Herrens Sang i et fremmed Land?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Dersom jeg glemmer dig, Jerusalem, da glemme mig min højre Haand!
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Min Tunge hænge ved min Gane, hvis jeg ikke kommer dig i Hu, hvis jeg ikke ophøjer Jerusalem over min højeste Glæde.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Herre! kom Edoms Børn i Hu efter, hvad de gjorde paa Jerusalems Dag, da de sagde: „Gører bart, gører bart indtil Grundvolden i den.”
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Babels Datter, du ødelagte! lyksalig den, som betaler dig din Løn for, hvad du lønnede os med.
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Lyksalig den, som griber og knuser dine spæde Børn imod Klippen.