< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
Na obali rijeka babilonskih sjeđasmo i plakasmo spominjući se Siona;
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
o vrbe naokolo harfe svoje bijasmo povješali.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
I tada naši tamničari zaiskaše od nas da pjevamo, porobljivači naši zaiskaše da se veselimo: “Pjevajte nam pjesmu sionsku!”
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Kako da pjesmu Jahvinu pjevamo u zemlji tuđinskoj!
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Nek' se osuši desnica moja, Jeruzaleme, ako tebe zaboravim!
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Nek' mi se jezik za nepce prilijepi ako spomen tvoj smetnem ja ikada, ako ne stavim Jeruzalem vrh svake radosti svoje!
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Ne zaboravi, Jahve, sinovima Edoma kako su u dan kobni Jeruzalemov vikali oni: “Rušite! Srušite ga do temelja!”
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Kćeri babilonska, pustošiteljice, blažen koji ti vrati milo za drago za sva zla što si nam ih nanijela!
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Blažen koji zgrabi i smrska o stijenu tvoju dojenčad!

< Zabura 137 >