< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
我們曾在巴比倫的河邊坐下, 一追想錫安就哭了。
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
我們把琴掛在那裏的柳樹上;
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
因為在那裏,擄掠我們的要我們唱歌, 搶奪我們的要我們作樂,說: 給我們唱一首錫安歌吧!
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
我們怎能在外邦唱耶和華的歌呢?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
耶路撒冷啊,我若忘記你, 情願我的右手忘記技巧!
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
我若不記念你, 若不看耶路撒冷過於我所最喜樂的, 情願我的舌頭貼於上膛!
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
耶路撒冷遭難的日子, 以東人說:拆毀!拆毀! 直拆到根基! 耶和華啊,求你記念這仇!
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
將要被滅的巴比倫城啊, 報復你像你待我們的,那人便為有福!
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
拿你的嬰孩摔在磐石上的, 那人便為有福!

< Zabura 137 >