< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
當我們坐在巴比倫河畔,一起想熙雍即淚流滿面。
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
在那地的楊柳間,掛起我們的琴絃。
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
因那些俘虜我們的,要我們唱歌,那些迫害我們的,還要我們奏樂:快些來給我們唱一支熙雍的歌!
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
但我們身處外鄉異域,怎能謳唱上主的歌曲?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
耶路撒冷!我如果將您忘掉,願我的右手枯焦!
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
我若不懷念您,不以耶路撒冷為喜樂,就寧願我的舌頭緊緊貼在我的上顎!
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
上主,求您記住厄東的子民,在耶路撒冷蒙難的時辰,他們曾喊叫說:拆毀,拆毀!夷為平地,一直見到基礎,
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
您只知破壞的巴比倫女子!誰若依照您加給我們的災痍,也焄樣報復於您,他就得福祺。
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
誰若抓起您的嬰兒幼子,摔在盤石上,他就得福祺。

< Zabura 137 >