< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Praise Yahweh - praise [the] name of Yahweh praise O servants of Yahweh.
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Who [are] standing in [the] house of Yahweh in [the] courts of [the] house of God our.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Praise Yahweh for [is] good Yahweh sing praises to name his for [it is] pleasant.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
For Jacob he has chosen for himself Yahweh Israel to possession his.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
For I I know that [is] great Yahweh and lord our more than all gods.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
All that he desires Yahweh he does in the heavens and on the earth in the seas and all [the] deeps.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
[he is] bringing up Clouds from [the] end of the earth lightning for the rain he makes [he is] bringing out wind from storehouses his.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
Who struck down [the] firstborn of Egypt from humankind unto animal[s].
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
He sent - signs and wonders in [the] midst of you O Egypt on Pharaoh and on all servants his.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
Who struck down nations many and he killed kings mighty.
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
To Sihon - [the] king of the Amorites and to Og [the] king of Bashan and to all [the] kingdoms of Canaan.
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
And he gave land their an inheritance an inheritance to Israel people his.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
O Yahweh name your [is] for ever O Yahweh remembrance your [is] to a generation and a generation.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
For he vindicates Yahweh people his and on servants his he has compassion.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
[the] idols of The nations [are] silver and gold [the] work of [the] hands of humankind.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
A mouth [belongs] to them and not they speak eyes [belong] to them and not they see.
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Ears [belong] to them and not they give ear also there not there [is] breath in mouth their.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Like them they will be [those who] make them every [one] who [is] trusting in them.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
O house of Israel bless Yahweh O house of Aaron bless Yahweh.
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
O house of the Levites bless Yahweh O [those] fearing Yahweh bless Yahweh.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
[be] blessed Yahweh - from Zion [who] dwells Jerusalem praise Yahweh.

< Zabura 135 >